Mahamud Abbas ya ziyarci zirin Gaza.
May 22, 2007Shugaban hukumar Palestinawa Mahamud Abbas, ya ziyarci zirin Gaza, a yunƙurin dakatar da hare-haren da yankin ke fuskantan daga Isra´ila, da kuma ɗorewar yarjejniyar tsagaita wutar da a ka cimma, tsakanin Hamas da Fatah.
Saidai saukar sa zirin ke da wuya, wasu jiragen sama masu durra angula na Isra´ila su yi amen wuta a kudancin Gaza, tare da jima mutane 4, mummunan raunuka.
Ranar 16 ga watan da mu ke ciki, Isra´la, ta ƙaddamar da wani gagaramin hari a Gaza, wanda ya zuwa yanzu, ya yi sanadiyar mutuwar mutane kusan 40.
Sannan a game da rikici tsakanin Hamas da Fatah, mutane fiye da 50 su ka kwanta dama, kamin cimma yarjejeniyar sulhu, a makon da ya gabata.
Mahamud Abbas, da Praministan Isma´ila Hanniey, za su gana nan gaba domin tantanawa a kann hanyoyin ƙarfafa zaman lahia a zirin Gaza, da ma Palestinu baki ɗaya.