Mahara sun kashe mutane da dama a Kwango
August 8, 2026
Maharan sun kuma yi wa mutanen garin fashi tare da kona musu gidajensu. Shugaban kungiyar farar hula ta birnin Mambasa, Marie-Noelle Anotane ta zargi kungiyar ADF da alhakin kai harin, inda ta ce maharan sun yi amfani da dabarun irin na kungiyar ne.
Karin bayani: Harin ta'addanci ya kashe mutanen Jamhuriyar Kwango kusan 20
Harin ya tilastawa mutane daukar zabi daya, zama a cikin fargaba a garin ko kuma kaura zuwa yankunan da cutar Ebola ke yaduwa a kasar. Kungiyar ADF, wadda ta samo asali daga Uganda kuma ta yi mubaya'a ga kungiyar IS a shekarar 2019, ta dade tana gudanar da ayyukanta a kan iyakar. Kana tana daya daga cikin kungiyoyi da dama da ke aiki a Kwango, inda suke yawan kai hare-hare kan fararen hula. A watan Yulin 2025, kungiyar ta kashe mutane 66 a gabashin kasar, harin da Majalisar Dinkin Duniya ta kwatanta da kisan kiyashi.