1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Majalisar Ɗinkin Duniya za ta gudanar da bincike a Libiya

May 18, 2012

Wata tawaga ta ƙwarraru na hukumar kare hakin bil adama na Majalisar Ɗinkin Duniya zata fara,za ta bincika maganar sojin haya a yaƙin Libiya

A fighter prepares to use his RPG during clashes between rival militias in the southern Libyan city of Sabha March 28, 2012. Picture taken March 28, 2012. REUTERS/Ibrahim Azagaa (LIBYA - Tags: POLITICS CIVIL UNREST CONFLICT)
Hoto: Reuters

Ƙwarrarun zasu fara gudanar da aikin bincikken domin tantance ko a kwai wasu sojojin haya na ƙasashen ƙetare da aka yin amfani da su a cikin yaƙin da aka gwabza a ƙasar.

Tawagar wacce zata fara ziyara a ranakun 21 zuwa 25 ga wannan wata bisa gayatar ƙasar ta Libiya, zata yi koƙarin haƙiƙance gaskiyar zarge zargen da aka sha yi akan wannan batu.Domin samar da hanyoyin magance matsalar, idan har hakan ya tabbata, kamar yadda shugabar tawagar Madame Faizal Pate ta baiyana.A cikin watan Satumba da ya gabata hukumar ta zargi sojojin hayar da ke mara wa tsoHuwar gwamnatin kanal Kaddafi bayada laifin keta hakin bil adama ta hanyar azabatar da jama'ar tare da karkashe wasu a birnin Tripoli.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane
Edita : Usman Shehu Usman