1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Lafiya

Tallafi ga Siriya bayan girgizar kasa

Lateefa Mustapha Ja'afar
February 14, 2023

Majalisar Dinkin Duniya ta kaddamar da bukatar neman tallafin dalar Amirka miliyan 397, domin taimakawa wadanda ibtila'in girgizar kasa ya rutsa da su a kasar Siriya.

Siriya | Harem | Girgizar Kasa | Tallafi
Mutanen da girgizar kasa ta shafa a Siriya na bukatar tallafin gaggawaHoto: Mahmoud Hassano/REUTERS

Sakatare janar na Majalisar Dinkin Duniyar Antonio Guterres ne ya sanar da bukatar neman tallafin a shalkwatar majalisar da ke birnin New York na Amirka, inda ya ce kudin da za a tara za su taimaka wajen kai dauki ga rayuwar mutane kusan miliyan biyar a Siriyan na tsawon watanni uku. Ya kara da cewa, majalisar na tattauna matakin karshe na adadin kudin da za a nema domin tallafawa wadanda girgizar kasar ta rutsa da su a Turkiyya da ke makwabtaka da Siriyan. Guterres ya kuma sanar da cewa Shugaba Bashar al-Assad na Siriya ya amince da kara bude wasu kan iyakokin kasar biyu da Turkiyya, domin bai wa jami'an agaji karin damar kai dauki ga wadanda bala'in ya shafa da yawansu ya kai miliyan tara. Mummunar girgizar kassar da ta afku a makon da ya gabata a kasashen Siriya Turkiyya dai, ta yi sanadiyyar rayukan dubban mutane a Siriyan tare da kara jefa wasu miliyoyi cikin halin tasku na neman tallafin jin-kai.