Makomar sulhun Hamas da Isra'ila a MDD
November 17, 2025
Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya, zai kada kuri’a kan sabon daftarin shirin zaman lafiya da shugaban Amurka Donald Trump, ya gabatar wa bangarorin Hamas da Isra'ila.
Isra'ila ta ce ita za ta zabi sojojin ketare don tsaron Gaza
Wannan matakin na zuwa ne bayan matsin lambar da Amurka ta yi, tare da yi hannunka mai sanda kan fargabar sake barkewar rikici, idan har ba akai gaza tabbatar da wani tsari mai dorewa a yankin Gaza, bayan da aka cimma yarjejeniyar sulhu tsakanin Hamas da Isra'ila a ranar 10 ga watan Oktoba.
Firaministan Isra'ila ya ba da umarnin kai hare-hare Gaza
Wata majiya ta tabbatar wa manema labarai ciki har da AFP cewa, kudurorin dake da muhimmanci a sabon daftarin sun kunshi girke sojojin kasa da kasa domin tabbatar da tsaron Gaza da za ta taimaka wajen tabbatar da tsaron yankin da batun tsare iyakokin Gaza da Isra'ila da Masar.
Hamas za ta mika gawar wani sojan Isra'ila
Kazalika shirin ya tanadi a rage karfin ikon Hamas da kwace makaman soji a hannun daukacin kungiyoyin da ba na gwamnati ba, sannan daftarin ya tanadi kafa gwamnatin wucin gadi a yankin har zuwa ranar 31 ga watan Disamban shekarar 2027.