1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Malamai sun kaurace wa azuzuwa a Jamhuriyar Nijar

Gazali Abdou Tasawa MAB
January 31, 2022

Malaman makarantu firamare da sakandaren Nijar sun shiga yajin aiki na kwanaki biyu domin neman gwamnati ta biya wasu bukatu da suka hada da biyan su a kan kari‚ da daukar su aiki na dindindin da biyan su kudaden alawus.

Niamey
Malamar makaranta na darasi a birnin Niamey na Jamhuriyar NijarHoto: DW/A. Mamane Amadou

Kungiyoyin malaman da suka hada da 'yan kwataragi da masu aikin dindindin sun tsunduma cikin wannan yajin aiki ne, bayan da zaman tattaunawar da suka yi da kwamitin ministocin da ke kula da harkokin ilimi a kasar Nijar ya watse ba tare da cimma matsaya ba, kan jerin bukatun malaman da ke a gaban gwamnati. Malam Mounkaila Halidou, memba a kawancen kungiyoyin malaman makarantun da ya shiga yajin aiki, ya ce jerin koke-kokensu sun hada da bukatar samun albashi a kan kari da kuma samu alawus da suke bin gwamnati.

Iyayen dalibai na son ganin gwamnati ta sansanta da malamai a NijarHoto: DW/A. Mamane Amadou

Kusann illahirin 'yan kwataragi wadanda sune kaso 80% na malaman makarantun boko ne suka kaurace wa makarantu, lamarin da ya sanya ba a yi karatu a akasarin makarntun ba. Wannan hali ya haddasa damuwa ga kungiyar iyayen yara 'yan makaranta wacce ta bukaci bangarorin da su gaggauta komawa kan teburin sulhu domin gano bakin zaren warware matsalar, kamar yadda Ibrahim Nalado, magatakardan kungiyar iyayen yara 'yan makaranta ta kasa ya bayyana.

Gwamnatin Nijar na neman shawo kan matsalolin malamai

Da yake tsokaci kan wannan yajin aiki, Ashana Hima da ke zama daraktan kula da ma'aikata a ma'aikatar ilimi ta kasa ya ce suna ci gaba da neman shawo kan wannan matsala cikin sauri. Wannan yajin aiki dai shi ne na farko da kungiyoyin malaman makarantun bokon suka shiga tun bayan soma karatun sabuwar shekara watanni uku da suka gabata.

Shugaban kasa Bazoum ya yi alkawarin bai wa fannin ilimi kulawaHoto: Presse- und Kommunikationsdienst der Präsidentschaft von Niger

'Yan kasa sun zura ido su ga yadda gwamnati za ta gaggauta shawo kan wannan matsala musamman ta la'akari da ikirarin da shugaban kasa Bazoum Mohamed yake yi na farfado da martabar ilimi a kasar Nijar. 

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani