1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Maleriya ta halaka mutane 4000 a Burundi

Yusuf Bala Nayaya
March 29, 2017

Sashin kula da huldodin jama'a a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa akwai mutane miliyan tara da suka harbu da rashin lafiya mai nasaba da maleriya a wannan kasa.

ihi-2012: Probanden mit Malaria infizieren
Hoto: Sanaria Inc

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa cutar maleriya ta halaka mutane 4000 tun bayan da cutar ta bulla a kasar Burundi. Wannan adadi dai ya zamo na ban mamaki duba da cewa ministan harkokin lafiya a  kasar a ranar 13 ga watan nan na Maris ya ce mutane 700 ne suka rasu ta sanadin cutar ta maleriya a kasar ta Burundi.

Sashin kula da huldodin jama'a a Majalisar Dinkin Duniya ya bayyana cewa akwai mutane miliyan tara da suka harbu da rashin lafiya mai nasaba da maleriya a wannan kasa da ke a Gabashin Afirka tun daga watan Janairu na shekarar 2016.

Akwai mutane miliyan 11 a wannan kasa ta Burundi da ta sake komawa rikici tun bayan hargitsin siyasa a shekarar 2015, ga matsala ta karancin abinci, abin da ya kara haifar da fargaba ta mutane da za su rasa rayuka. A cewar rahoton na Majalisar Dinkin Duniyar mutum guda cikin goma a Burundi na fama da kansa idan ana magana ta abincin da zai kai bakinsa.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW