Mali na bukatar sojojin mayar da martani
October 8, 2014Talla
Kasar Mali ta bukaci Kwamitin Sulhun Majalisar Dinkin Duniya da ta aika mata da sojojin mayar da martanin gaggawa su taimaka mata wajen kwantar da hare-haren da ake kaiwa dakarun wanzar da zaman lafiyar Majalisar Dinkin Duniyar ba kakkautawa a yankin arewacin Mali, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 31.
Ministan harkokin wajen Mali Abdoulaye Diop ya fadawa Kwamitin mai mambobi 15 cewa tilas ta dauki matakan gaggawa, wadanda za su tabbatar da cewa Majalisar ta gudanar da ayyukan da za su kare muradunta na kula da rayukan fararen hula, musamman ganin yadda dakarun wanzar da zaman lafiyan ke jin shi a jika wajen gudanar da ayyukansu