1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali na neman 'yan kasashen ketare da aka sace ruwa-a-jallo

Abdoulaye Mamane Amadou
September 25, 2025

Gwamnatin mulkin soja a Mali, ta sanar da cewa an sace baki 'yan kasashen waje uku a wajen babban birnin kasar Bamako a makon jiya

Janar Assimi Goita shugaban kasar Mali
Janar Assimi Goita shugaban kasar MaliHoto: Pavel Bednyakov/AFP

Gwamnatin Mali ta sanar da sace wasu 'yan asalin Hadaddiyar Daular Larabawa biyu da wani dan Iran guda a makon da ya gabata a kusa da Bamako babban birnin kasar.

Ficewar kasashen AES daga kotun ICC

A cikin wata sanarwar da ma'aikatar tsaron cikin gidan Mali ta fitar a ranar Alhamis, gwamnatin ta ce an sace mutanen ne a makon jiya, kuma tana iya kokarinta domin ganin ta kubutar da su.

Kungiyar Kasashen yanki Sahel ta cika shekaru

Tun a shekarar 2012 kasar Mali da yanzu haka ke karkashin mulkin soja ke fama da mummunar matsalar tsaro, wacce ta samo asali daga tashe-tashen hankula na kungiyoyi masu tayar da kayar baya masu alaka da Al-Qaïda da IS, lamarin  da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama ciki har da mata da kananan yara.