1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Abzinawa 'yan aware sun karyata gwamnatin sojan Mali

Abdoulaye Mamane Amadou
November 22, 2023

Kwanaki bayan karbe iko da yankin Kidal tungar 'yan awaren arewacin Mali, mayakan sun karyata shelar gwamnatin mulkin soja na gano gawarwaki a kabari guda

Mali Kidal | Rebellengruppe CMA
Hoto: SOULEYMANE AG ANARA/AFP/Getty Images

Mayaka 'yan aware na Abzinawan Mali sun karyata gwamnatin sojan kasar da ta zargi samun gawarwakin dumbin mutane a kabari guda, jim kadan bayan dakarunta suka karbe iko da birnin Kidal da ke zama tungar 'yan tawayen a makon jiya.

Mayakan sun bayyana a cikin wata sanarwa da cewa shelar wani yunkurin gwamnatin Bamako ne kawai na shafa musu kashin kaji, tare da boye ainihin kisan kiyashin da suka yi a yankin a kokarinsu na rige-rigen karbe iko da yankin Kidal da ke karkashin kulawar 'yan tawaye, tun bayan soma barkewar fitina a wannan kasa.