1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mali za ta mutunta yarjejeniyar Algiers

February 16, 2023

Gwamnatin mulkin sojin Mali ta bayyana kudirinta na mutunta yarjejeniyar zaman lafiya da a baya aka cimma da Abzinawa 'yan tawaye na arewacin kasar a shekarar 2015 a birnin Algiers.

Symbolbild I Frieden Mali
Hoto: Habibou Kouyate/AFP/Getty Images

Wannan mataki ya biyo bayan tangal-tangal da yarjejeniyar ke yi sakamakon aniyar 'yan twayen Azawad na yin fatali da ita, duk da kokarin da kasashen Afirka ke yi don shiga tsakanin bangarorin biyu da ke gaba da juna.

Tun a shekarar 2015 ne gwamnatin Mali da 'yan tawaye suka amince a kasar Aljeriya da kawo karshen yunkurin raba kasar gida biyu, sai dai ci gaba da gwabza fada da 'yan tawayen ke yi ya bazu zuwa tsakiyar Mali da kasashen Nijar da Burkina Faso da ke makwabtaka.

Gwamnatin sojin ta Mali ta ce sojojinta na shirin dawo da yankin Kidal da ke hannun 'yan tawaye na CMA a karkashi ikonta.

Amma a halin yanzu hukumomin Aljeriya na kokarin shawo kan bangarorin na Mali da ba sa jituwa da su kai zuciya nesa.