1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Martani kan kara dakarun Faransa a Afirka

Abdoulaye Mamane AmadouMarch 12, 2015

Tun bayan da gwamnatin Faransa ta sanar da manufarta na tura karin dakaru zuwa yammacin Afirka domin yakar Boko Haram ne dai, mahawara ta kunno kai a Nijar.

Afrika Nigeria Niger & Tschad Offensive gegen Boko Haram
Hoto: Reuters/E. Braun

A Jamhuriyar Nijar, masana da ma kungiyoyin kare hakkin jama'a na ci gaba da tofa albarkacin bakinsu kan yiwuwar karin dakarun kasar Faransa a kasashen Afirka, musamman ma a Nijar domin yaki da 'yan Boko Haram.

Ra'ayoyi dai sun banbanta kan kafa rundunonin na Faransa. A yayin da wasu ke yabawa da kokarin da sojojin ke yi, wasu kuwa na mai kallon batun tamkar wani sabon salo ne na mulkin mallaka.

Tun a farkon wannan shekarar ce dai sojojin Kamaru da Chadi da Nijar da kuma Benin, suka fara taimaka wa takwarorinsu na Najeriya a kokarinsu na kawo karshen mayakan tada kayar baya na Boko Haram, bayan da kungiyar ta karbe madafan ikon wasu yankunan kasar, tare da fara kaddamar da hare-hare a kan garuruwan da ke kan iyakokin kasashe makwabta.

A yanzu haka dai Faransa na da adadin sojojinta 3,000 a yankin, ban da wasu dakaru na musamman, wadanda ke jibge a Mauritaniya daga yammaci zuwa kudancin Libiya, wadanda aka dora wa alhakin farautar mayakan kungiyar Al-qaida.