1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Martanin Burtaniya kan harin Isra'ila a Siriya

May 5, 2013

Sakataren harkokin wajen Burtaniya William Hague ya ce harin da Isra'ila ta kai kasar Siriya na nuna irin mastalar da ke akwai ta tabarbarewar tsaro a yankin gabas ta tsakiya.

EDITOR'S NOTE: REUTERS CANNOT INDEPENDENTLY VERIFY THE CONTENT OF THE VIDEO FROM WHICH THIS STILL IMAGE WAS TAKEN The sky is lit up after an explosion at what Syrian state television reported was a military research centre in Damascus, in this still image taken from video obtained from a social media website by Reuters on May 5, 2013. Powerful explosions struck the outskirts of Damascus early on Sunday, sending columns of fire into the night sky, and Syrian state television said Israeli rockets had struck a military facility just north of the capital. An Israeli overnight strike in Syria targeted Iranian-supplied missiles to Lebanese guerrilla group Hezbollah, a Western intelligence source said on Sunday. Israel declined to comment on the attack. REUTERS/Social Media/Handout via Reuters TV (SYRIA - Tags: CONFLICT MILITARY) ATTENTION EDITORS � THIS PICTURE WAS PROVIDED BY A THIRD PARTY. REUTERS IS UNABLE TO INDEPENDENTLY VERIFY THE AUTHENTICITY, CONTENT, LOCATION OR DATE OF THIS IMAGE. NO SALES. NO ARCHIVES. FOR EDITORIAL USE ONLY. NOT FOR SALE FOR MARKETING OR ADVERTISING CAMPAIGNS. THIS PICTURE IS DISTRIBUTED EXACTLY AS RECEIVED BY REUTERS, AS A SERVICE TO CLIENTS
Damaskus Angriff Israel Beschuss SyrienHoto: Reuters

Mr. Hague ya ambata hakan ne a wannan Lahadin inda ya kara da cewar ya kyautu a ce an janye takunkumin nan na makamai da aka kakabawa 'yan tawayen Siriya wanda ke rajin kawar da shugaba Assad daga gadon mulki.

Yayin da sakataren na harkokin wajen Burtaniya ke wadannan kalamai, a hannu guda Iran kira ta yi da a juyawa Isra'ila baya sakamakon harin da ta kai wa Siriya inda ta ce a shirye ta ke da ta tallafawa dakarun gwamnatin Siriya da horo irin na dabarun yaki.

Da sanyin safiyar yau ne dai jiragen yakin Isra'ila su ka kai jerin hare-hare kan wata cibiya ta bincike kimiyya da harkokin tsaro ta kasar ta Siriya, lamarin da ya sanya wajen yin dameji kamar yadda wanda su ka shaida harin su ka bayyana wa manema labarai.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammad Nasiru awal