Martanin Afrika ta Kudu a kan ganawar Trump da Ramophosa
May 22, 2025
Ganawar da shugabannin biyu suka yi a jiya Laraba na da nufin gyara alakar da ta yi tsami tun bayan da Donald Trump ya hau karagar mulki a watan Janairu, inda daga baya ya yi barazanar kakaba harajin kasuwanci da kuma korar jakadan Afirka ta Kudu.
A yayin taron dai an nuna wani faifan bidiyo wanda ya nuna shugaban wata jam'iyyar adawa mai tsatsauran ra'ayi yana rera wakar gwagwarmayar yaki da wariyar launin fata,.
Trump ya kuma sake nanata zarge-zargen da ba shi da tushe balle makama da ke cewa Afirka ta Kudu na kwace filaye daga wasu tsirarun fararen fatar kasar, zuriyar mazauna kasar Holland, wadanda a zahiri ke mallakar fiye da kashi uku cikin hudu na filayen kasuwanci.
'Yan kasar da dama suka kalli tattaunawara kai tsaye, tare da yin alfahari shugaba Ramaphosa da da tawagarsa.