Miliyoyin masu haya a gidajen da aka kayyade musu farashi tun shekaru 70 da suka gabata a Masar, na fuskantar barazanar fitar da su da karfi daga gidajen.
Shugaban kasar Masar Abdel Fattah al-SisiHoto: JAVIER SORIANO/AFP/Getty Images
Talla
Wannan fargaba da mazauna gidan hayar ke ciki, na zuwa ne sakamakon wata doka da majalisar dokokin Masar ta amince da ita take jiran shugaban kasar ya rattaba mata hannu. Kimanin mutane miliyan 20 da ke zaune a gidajen haya kusan miliyan uku da a aka kayyade musu farashi tun shekaru 70 da suka gabata ne, wannan doka da ta yi gyaran fuska za ta shafa. A tsohuwar dokar haya da ake aiki da ita tun shekaru kimanin 70 din da suka gabata, mai haya a wancan lokacin zai bayar da makudan kudin da sun kai daya bisa ukun kudin gidan na hakika domin ya zauna a gidan shi da ya'yansa manya har iya bakin ransu yadda za su dinga biyan tabbataccen kudin hayar da bai taka kara ya karya a wancan lokacin ba ballantana a yanzu. Wafa Ashur da ta gaji daya daga cikin gidajen hayar da aka bayar da hayarsu a kan tsohon tsarin dokar haya ta ce, idan wannan dokar ta fara aiki za ta fara karbar kudin hayar da suka dace da darajar gidanta ko kuma a ba ta damar komawa gidan ta zauna bayan fitar da 'yan hayar cikinsa.
Bayan juyin juya halin Masar: Murkushe fatan 'yan kasa
Bayan da guguwar neman sauyi ta yi awon gaba da Mubarak, shi ma Mursi na 'Yan Uwa Musulmi da ya gajeshi an hambarar da shi. Al-Sisi ne ke fada a ji a Masar a yanzu. Sai dai kungiyoyin fararen hula na dandana kudarsu.
Hoto: AFP/Getty Images/K. Desouki
Haramta tunawa da guguwar neman sauyi
A ranar Lahadi 25 ga watan Janairu aka cika shekaru hudu da barkewar zanga-zangar kin jinin gwamnatin Hosni Mubarak. Kimanin mutane 800 ne suka rasa rayukansu a lokacin da guguwar neman sauyi ta kada a shekara ta 2011. Sai dai ba a gudanar da biki ko addu’ar tunawa da wadanda suka mutu ba. Maimakon haka hukumomin Masar sun killace dandalin Tahrir bisa dalilai da suka danganta da na tsaro.
Hoto: Reuters/M. Abd El Ghany
kashe-kashe a ranar tunawa da baya
Wannan hoton ya shiga cikin tarihin ranar tunawa da juyin juya hali a Masar. Shaima Al-Sabbagh ta zo da mijinta dandalin Tahrir don karrama ranar da zanga-zangar neman sauyi ta barke a 2011. Amma kuma ba ta koma da rai ba. Masu zanga-zanga suka ce 'yan sandan ne suka harbeta. Yayin da gwamnati ta zargi 'yan bindiga da wannan aika-aika. Mutane da dama ne suka mutu a wannan rana ta nuna alhini.
Hoto: Reuters/Al Saabi
Zanga-zanga ta haramta a Masar
Hukumomin Masar ba su tsaya a kashe-kashe kawai ba. 'Yancin fadan albarkanci baki da na gangami ma sun samu illa. Wata doka da ake cece-kuce a kanta ta haramta gudanar da duk wani gangamin da ba a amince da shi ba. An kama shugabannin kungiyoyin fararen hula da dama tare da dauresu. Su ne kashin bayan juyin juya hali na shekara ta 2011.
Hoto: Reuters/M. Abd El Ghany
Juyin juya hali na biyu bayan na Mubarak
Fata na gari ne ke tattare da 'yan Masar lokacin juyin juya hali na 2011. Faduwar gwamnatin Mubarak ya bayar da damar shirya zabe bisa tafarkin demokaradiya tare da samar da sabon kundin tsarin mulki. Mohamed Mursi na 'yan Uwa Musulmi ne ya zama shugaban kasa. Sai dai take-takensa ya sa an ta zanga-zanga a 2013. Abdel Fattah Al-Sissi wanda shi ne shugaba na yanzu ya hambarar da shi daga mulki.
Hoto: picture-alliance/dpa
Mulkin kama karya ya dawo a Masar?
‘Yan Masar da dama sun yi fatan ganin Al-Sisi ya magance matsalar koma bayan tattalin arziki da kuma ta tsaro da suka addabi kasarsu. Sai dai masu rajin kare hakkin dan Adam na fargabar sake mayar da kasar kan tafarkin mulkin kama karya maimakon na demokadariya.
Hoto: Markus Symank
Farautar 'yan Kungiyar 'Yan Uwa Musulmi
Tun kafin a zabeshi shugaban kasa Al-Sisi ya sanya Kungiyar 'yan Uwa Musulmi a rukunin kungiyoyi 'yan Ta'adda. Wata kotu a Al-Minja ta yanke wa 'ya'yan kungiyar 529 hukuncin kisa. Hakazalika a watan Afirilu alkali ya yanke ma wasu karin 683 irin wannan hukunci. An sassauta hukuncin da dama daga cikinsu zuwa ga na daurin rai da rai, yayin da ake ci gaba da nazarin sauran hukunce-hukuncen.
Hoto: picture-alliance/AP Photo
Kungiyoyin fararen hula na shan zargi
Matsin lamba a kan 'yan luwadi da madigo da kuma wadanda ba ruwansu da addini sun zame wa hukumomin Masar manufofi na addini. Tsare shugabannin kungiyoyin fararen hula da 'yan jarida da kuma lawyoyi ba tare da kwakkwaran dalili ba ya zama ruwan dare. kamar yadda kuke gani a wannan hoto, haka ya faru da ma'aikacin tashar Al-Jazeera.
Hoto: picture-alliance/dpa/Elfiqi
An sa kungiyoyi masu zaman kansu a gaba
Al-Sisi ya rattaba hannu a kan dokoki da dama da nufin rage wa kungiyoyin fararen hula karfin fada a ji, inda ya tsaurara dokokin. Za a gurfanar da duk wata kungiya da ake zargin ta samu kudi daga kasashen waje ko kuma ta ke neman cin amanar kasa. Da ma dai karkashin mulkin kama karya na Mubarak an ta amfani da shigen wannan doka wajen musgunawa kungiyoyi masu zaman kansu.
Hoto: dapd
Shari'ar Mubarak da 'ya'yansa
A watan Nuwamba, wata kotu ta wanke Hosni Mubarak daga laifukan marar hannu a kashe masu zanga-zanga a 2011. Daya bayan daya, ana ta wankeshi daga jerin laifuffukan da ake zarginshi da aikatawa. Wata kotu na sake sauraran kararsa da aka shigar kan badakalar cin hanci da karbar rashawa. Su ma 'ya'yan Mubarak wato Alaa da Gamal, an wankesu.
Hoto: AFP/Getty Images/K. Desouki
Hotuna 91 | 9
Gwamnati dai ta ce za ta rarraba sababbin gidaje ga wadanda suka yadda suka bar tsofafin gidajen da suke biyan kudin hayar jeka-na-yi-kan da bai karuwa tun shekaru 60, idan suka fita daga gidajen domin radin kansu a kokarin da take ta raba gardama tsakanin masu gidajen hayar da 'yan hayar da kowannansu ke zargin cewa ana so ne a cuce shi. To sai dai da dama daga cikin 'yan hayar sun dage kan cewa, ba za su bar cikin birni da suka rayu shekara da shekaru ba. Shi kansa Shugaba Abd al-Fattah al-Sisi da ake jiran ya ranttaba hannu a kan wannan sabuwar doka ya ce, dola ce ta sanya shi daukar matakin kawo karshen dokar gidajen hayar da ta jima tana janyo rikici tsakanin 'yan haya da masu gidajen hayar. Tun daga shekarar 1960 ne aka fara cin moriyar wannan tsarin hayar a kasar ta Masar, wadda kuma ke janyo cece-kuce.