1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masar ta katse ba da makamashi ga Israi' la

April 23, 2012

A wani mataki da zai kai tsamin dangatakar tsakanin Masar ta Israila, Masar ta soke yarjejeniyar sayr wa Israi'la iskar gas.

epa02564963 A view showing huge flames erupting from a blast at Egyptian gas pipeline supplying Israel and Jordan in Al-Arish, Egypt, 05 February 2011. An explosion occurred Saturday at an Egyptian pumping station in the Sinai Peninsula supplying natural gas to Israel and Jordan. Egyptian state television said the explosion was a 'terrorist operation' and blamed 'saboteurs' for the incident, saying they had taken advantage of the country's ongoing political unrest. EPA/STR
Hoto: picture-alliance/dpa

An samu kunnowar sabuwar takkadama tsakanin Masar da Isra'ila bayan da kamfanin gas din kasar Masar ta sanar da ske yarjejeniyar da ta kulla tare Isra'ila akan cinikin gas. Shi dai kamfanin gas din ya bayyanar da rashin biye wa yarjejeniyar a matsayin dalilinsa na daukar wannan mataki. Hakazalika ma'aikatar man fetur kasar ta Masar ta sanar da dakatar da ba wa Isra'ila mai a sakamakon abin da ta kira hare-haren da ake zargin kungiyoyin kishin Islama da kaiwa akan bututan mai da ke a yankin Sinai. Kasar Masar ita ce ke samar wa Isra'ila kashi 40 daga cikin dari na iskar gas da take bukata. Tuni jami'in gwamnatin Isra'ila ya yi kashedi game da katsewar wutar lantarki a lokacin rani .

Mawallafiya: Halima Balaraba Abbas
Edita: Abdullahi Tanko Bala