Masar za ta shirya taro kan makomar Gaza
October 11, 2025
Hukumomin Masar sun ce Shugaban Amurka Donald Trump shi ne zai kasance babban bako a wajen taron tare da takwaransa na Masar Abdel-Fattah al-Sissi.
Ma'aikatar Harkokin Wajen Masar ta ce tuni Ministan Harkokin Wajen Kasar Badr Abdel-Atti da Sakataren Harkokin Wajen Amurka Marco Rubio suka fara tattaunawa ta wayar tarho domin fara aiwatar da daftarin gudanar da taron.
Karin bayani:Masar ta shirya taron zaman lafiya kan rikicin Gaza
Shugabannin kasashen yammacin duniya da dama ne ake sa ran zasu hakarci taron na Masar kan Gaza. Kazalika Shugaba Al-Sissi ya gayyaci Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz domin ya shaida aiwatar da yarjejeniyar.
Karin bayani: Isra'ila ta amince da tsagaita wuta a yakin Gaza
A wani labarin kuma babban kwamandan rundunar tsaron Amurka ya isa Gaza, inda ya tabbatar da cewa babu wani sojin Amurka guda da ke yankin.