SiyasaTunusiya
Al'umma a Tunisiya sun bukaci a saka ranar zabe
May 12, 2024![Tunesien | Umgang mit Migranten](https://static.dw.com/image/68917051_800.webp)
Talla
Masu boren ko baya ga haka sun kuma bukaci a gaggauta saka ranar da za a gudanar da babban zabe a kasar da ke arewacin nahiyar Afirka.
Boren na zuwa ne a daidai lokacin da al'umma ke tsaka da fama da matsin tattalin arziki da ma matsalolin siyasa da suka yi wa kasar katutu.
Karin bayani: Shekaru 12 da juyin-juya halin Tunisiya
A baya hukumar zaben kasar ta yi alkawarin gudanar da zabe a kan lokaci, to sai dai har yanzu da wa'adin Shugaba Kais Saied da aka zaba a shekarar 2019 ke gaba da cika, hukumar ta gaza saka ranar yin zabe.
Masu boren sun yi kira da a tsaftace fagen siyasar kasar da ma ba da damar fadin albarkacin baki.