1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matakin ICC kan shari'ar shugaban Kenya

October 18, 2013

Kotun da ke hukunta laifukan yaki ta kasa da kasa ta ICC da ke birnin Hague na kasar Holland ta ce shugaban Kenya zai iya kauracewa zaman shari'ar da za a masa.

Kenya's President Uhuru Kenyatta makes his statement to the nation at the State House in Nairobi on September 22, 2013, following the overwhelming numbers of casualties from the Westgate mall shooting in the Kenyan capital. Kenyan President Uhuru Kenyatta said Sunday a nephew and his fiancee were among the 59 people confirmed killed in an ongoing siege in an upmarket shopping mall by Somali militants. AFP PHOTO / JOHN MUCHUCHA (Photo credit should read John Muchucha/AFP/Getty Images)
Uhuru Kenyatta Ansprache RedeHoto: John Muchucha/AFP/Getty Images

Kotun hukunta laifukan yaki ta ICC ta kasa da kasa da ke birnin Hague na kasar Holland ta amince cewar ba lallai ne shugaban Kenya Uhuru Kenyatta da ya hallarci zaman kotun ba a shari'ar da za ta fara yi masa cikin watan gobe, dangane da zargin da ta ke masa na aikata laifukan yaki biyo bayan rikicin zaben da aka yi a kasar cikin shekara ta 2007.

Kotun dai ta bayyana hakan ne a wannan Juma'ar bayan da alkalanta suka yi wani zama na musamman kan batu kuma suka bada amincewarsu.

Alkalan dai sun ce sun dau wannan mataki ne domin baiwa shugaba Kenyatta damar gudanar da aikinsa na shugaban kasa wanda ke cike da hidimomi.

Wannan mataki na kotun ta ICC dai na zuwa ne mako guda bayan da kungiyar kasashen Afrika ta AU ta ta yi wani taro inda ta amince cewar shugabannin da ke kan mulki ba za su hallarci zaman kotun ba.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Mohammad Nasiru Awal