Matar Trump ta jagoranci taron kwamitin sulhu na MDD
March 3, 2026
Talla
A taron da ta jagoranta a birnin New York a ranar Litinin ta bukaci a dauki matakai domin samar da zaman lafiya domin kyautata rayuwra kananan yara. Ta jagoranci taron a yayin da Amurka ta karbi shugabancin kwamitin daga watan nan na Maris. Taron ya mayar da hankali kan lafiyar kananan yara, fasahar zamani da ilimi a yankunan da ake fama da rikici.
Melania ta kuma jajanta wa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a rikice-rikice, tana mai cewa Amurka na tare da yara a fadin duniya. Ta jaddada cewa ilimi na da muhimmanci wajen hana rikici da kuma gina zaman lafiya mai dorewa.
Sai dai ba ta yi tsokaci kan harin da Amurka da Isra'ila suka kai Iran da abin da ya biyo bayansa ba.