1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Matsalar karancin abinci a Sudan

January 5, 2012

Dubban mutanen a kasar Sudan na fiskantar masifar karancin abinci sakamakon fada tsakanin sojan gwamnati da yan tawayen SPLM

In this photo taken Thursday, June 9, 2011 and provided by the United Nations Mission in Sudan (UNMIS) on Friday, June 10, 2011, residents gather outside the UNMIS sector headquarters after fleeing fighting in Kadugli, the capital of South Kordofan, Sudan, Thursday, June 9, 2011. The United Nations and international aid groups say the spreading conflict between North and South Sudan is driving thousands more people from their homes and U.N. spokeswoman Elisabeth Byrs says aid agency offices in Kadugli have been looted and most local and international aid staff have fled the Kadugli area. (AP Photo/UNMIS, Paul Banks) EDITORIAL USE ONLY, NO SALES
Yan gudun hijira a jahar Kordofan kasar SudanHoto: AP

Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa ta samu rahotanni dake bayyana tsanantar rashin abinci mai gina jiki ga al'ummar da ke kan iyakar kasar Sudan da suke tserewa tashin hankalin da ake yi, inda sojojin gwamnati ke yakar yan tawayen SPLM wani babban jami'in MDD yace al'ummar da ta tserewa fadar sun bayyana tsananin rashin abince da suke fiskanta, musamman a yankunan dake hannun yan tawayen SPLM. Tun a watan Juni fada ta barke tsakanin sojan gwamnatin Sudan ta kudu da yan tawayen SPLM a kudancin jahar Kordofan, kuma a yanzu ya yadu zuwa jihar Blue Niles. MDD ta yi kiyasin cewa mutane dubu 400 suka tsere daga gidajensu, kana fi ye da dubu 80, suka shiga Sudan ta kudu. Sudan ta kudu dai tun a watan Juli ta samu yancin kai, amma bata kai ga samun cikakken zaman lafiya ba.

Mawallafi: Usman Shehu Usman

Edita:        Umaru Aliyu