1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

'Yan bindiga sun kashe mutane 30 a Katsina

Abdourahamane Hassane
February 16, 2020

'Yan bindiga sun halaka mutane guda 30 a wani harin da suka kai a arewa maso gabashin Najeriya.

Nigeria Polizei
Hoto: Getty Images/AFP/P. Utomi Ekpei

Mutanen wadanda ke bisa babura su kusan guda goma sun kai hare-haren a kauyukan Tsauwa da Dankar da ke cikin Jihar Katsina inda suka yi harbin kan mai uwa da wabi a kan jama'a suka kashe mutane 30. Kakakin 'Yan sanda na Katsina Gambo Isa ya ce 'yan bindigar sun kashe mutane 21 a Tsauwa kafin su harbe tara a Dankar. Gwamnatin Jihar Katsina ta baza 'yan sanda a kauyukan wadanda suka soma gudanar da bincike, tuni da suka kama wani mutumin da ake zargi yana daga cikin maharan.