Matsalar yinwa a Tchad
March 30, 2007Talla
Hukumar samar da abinci ta Majalisar Ɗinkin Dunia, ta bayyana matsanacin halin ƙarancin abinci, da al´ummomin ƙasar Tchad, su kimanin dubu 130 ke fuskanta, a sanadiyar halin gudun hijira ,da su ka tsinci kan su a ciki.
Kakakin hukumar, Christiane Berthiaume ta ce dukkan wannan mutane, sun ƙaura daga gidajen su, a dalilin tashe-tashen hankulla a yankin Darfur na ƙasar Sudan.
Domin kawo tallafi ga wannan jama´a, hukumar na bukatar a ƙalla dalla milion 7 da rabi, ta fannin abinci barguna da magungunna.
Bayan mutanen Ƙasar Tchadin, hukumar na kai agaji ga ƙarin yan gudun hijira Sudan, kussan dubu 250, da ke tsugune a iyakar Tchadi.