Matsayin tsarin mulkin Najeriya dangane da barin jam'iyyar siyasa
January 21, 2014![Nationalversammlung in Abuja, Nigeria](https://static.dw.com/image/16794744_800.webp)
Talla
Tsarin mulkin Najeriya ya bai wa ko dai 'yan majalisar dokoki ko kuma gwamnoni damar ficewa daga jam'iyyar da aka zabesu a karkashinta, muddin dai jam'iyyar tana fuskantar rigingimu ko kuma ta rushe.
Masana harkokin shari'a sun nunar da cewar inda za a fuskanci matsala shi ne idan jam'iyya na dunkule, babu rarrabuwar kawuna a cikinta.
Domin karin bayani, za ku iya sauraren shirin a kasa.
Mawallafi : Saleh Umar Saleh
Edita : Abdourahamane Hassane