1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

An kashe sojojin Burkina Faso

Abdul-raheem Hassan MNA
January 29, 2020

Hukumomin tsaron a Ouagadougou sun tabbatar da mutuwar dakarun gwamnatin kasar shida tare da batar wasu da dama bayan wani sabon hari da ake zargin mayakan jihadi da kaddamarwa.

Afrika 2019 | Burkina Faso | Soldaten im Einsatz in Bobo-Dioulasso
Hoto: Imago Images/ZUMA Press/D. White

Mayakan sun sa bam a jikin motar sojojin tare da bude musu wuta yayin da suke sintiri daga garin Madjoari zuwa Pama da ke gabashin lardin Kompienga na kasar ta Burkina Faso.

Wannan sabon harin ya faru bayan wani mummunan hari da ya halaka fararen hula akalla 50. Kungiyoyin da ke gwagwarmaya da makamai sun kashe mutane akalla 800 tare da tilasta kusan 6,000 gudun hijira a Burkina Faso tun bayan tsanantar matsalar rashin tsaro a 2015, abin da ake ganin ya fara shafar makotan kasashe kamar irin su Mali.