1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Mayakan RFS na Sudan sun halaka mutane 40

Suleiman Babayo ZUD
November 5, 2025

Fararen hula kimanin 40 sun halaka sakamakon harin mayakan RSF na Sudan, abin da ke nuna irin mawucin hali da fararen hula suka shiga sakamakon rikicin da ke faruwa tsakanin bangarorin biyu.

Mayakan RSF
Mayakan RSFHoto: Rapid Support Forces/AFP

Hari da mayakan RSF na Sudan suka kai ya hallaka kimanin fararen hula 40 a garin el-Obeid da ke zama helkwatar jihar Arewacin Kordofan, kamar yadda kafofin yada labaran kasar suka ruwaito. Wannan bayan rahotanni kan irin ta'asa da mayakan na RSF ke aikatawa a yakin da aka kwashe shekaru biyu ana fafatawa.

Lamura sun rincabe

Sojojin gwamnatin Sudan ba duba makaman da suka kwaceHoto: AP Photo/picture alliance

Ofishin jami'in Majalisar Dinkin Duniya mai kula da kare hakkin dan Adam ya nuna damuwa kan abin da yake faruwa a Kordofan lokacin da ake ganin ganin yadda makwabtan na Darfur suka shiga mawuyacin hali a hannun mayakan na RSF.

A shekara ta 2023 fada ya barke tsakanin sojojin gwamnatin Sudan da mayakan rundunar RSF, inda kiyasin hukumar Lafiya ta Duniya ya nuna kimanin mutane dubu-40 suka mutu a rikicin da ke faruwa, yayin da wasu kimanin milyan 12 suka tsere daga gidajensu, sannan wasu sama da milyan 24 ke fuskantar matsalar karancin abinci.