MDD: Mutane 606 sun bace a Bahar Maliya
February 23, 2026
Talla
Wannan shi ne rahoto mafi muni da aka samu a farkon shekara a Bahar Maliyar tun bayan da Hukumar kula kaurar jama'a ta duniya ta fara daukar alkalumma a shekarar 2014. Wani kakakin hukumar na cewa, a kalla mutane 30 ne suka yi batan dabo bayan da kwale-kwalensu da ya doshi Girka ya kife a wannan Asabar din. Yawancin fasinjojin kananan yara ne 'yan kasashen Sudan da Masar.
Ko a shekarar da ta gabata an ci gaba da ganin kwarar bakin haure daga kasar Libiya a wani mummunan yunkuri na isa Girka da ke cikin kungiyar Tarayyar Turai.
Hukumar ta IOM ta yi kira da a kara hadin gwiwa a yankin tare da karfafa ayyukan bincike da ceto a tsakiyar tekun sakamakon cin zarafin da masu safarar mutane ke yi.