1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD: Mutane 606 sun bace a Bahar Maliya

February 23, 2026

Rahoton Hukumar Kula da 'Yan gudun Hijira ta Majalisar Dinkin Duniya na nuni da cewa, a kalla bakin haure 606 ne suka mutu ko suka bace a tekun Bahar Maliya a shekarar 2026.

Jirgi dauke da wasu bakin haure da aka ceto a Crete yayin da suke kokarin dosar Girka
Jirgi dauke da wasu bakin haure da aka ceto a Crete yayin da suke kokarin dosar GirkaHoto: Costas Baltas/Anadolu Agency/IMAGO

Wannan shi ne rahoto mafi muni da aka samu a farkon shekara a Bahar Maliyar tun bayan da Hukumar kula kaurar jama'a ta duniya ta fara daukar alkalumma a shekarar 2014. Wani kakakin hukumar na cewa, a kalla mutane 30 ne suka yi batan dabo bayan da kwale-kwalensu da ya doshi Girka ya kife a wannan Asabar din. Yawancin fasinjojin kananan yara ne 'yan kasashen Sudan da Masar.

Ko a shekarar da ta gabata an ci gaba da ganin kwarar bakin haure daga kasar Libiya a wani mummunan yunkuri na isa Girka da ke cikin kungiyar Tarayyar Turai.

Hukumar ta IOM ta yi kira da a kara hadin gwiwa a yankin tare da karfafa ayyukan bincike da ceto a tsakiyar tekun sakamakon cin zarafin da masu safarar mutane ke yi.