1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

MDD na son Rasha ta sake tunani kan abinci

July 25, 2023

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres ya bukaci Rasha da ta sake komawa ga yarjejeniyar nan ta fitar da kayan abinci ta tekun Bahar al-Aswad.

Hoto: Thomas Mukoya/REUTERS

Antonio Guterres ya ce rashin komawar Rasha ga yarjejeniyar da ta janye daga ciki a farkon wannan wata, zai sanya kasashen da suka dogara da kayan abincin da ke fita daga Ukraine ta wannan tekun cikin yanayi mai muni.

Ya yi wannan kira ne a jawabin da ya gabatar lokacin taro kan lamarin abinci a duniya da aka yi a birnin Rome na kasar Italiya.

Jagoran na Majalisar Dinkin Duniya ya jaddada matsayin kasashen Rasha da Ukraine wadanda a yanzu ke yaki ta fuskar samar da abinci a duniya.

Akasarin hatsi da Ukraine ke fitarwa ta tekun dai na zuwa kasashen Afirka ne da na Gabas ta Tsakiya da ma wasu sassa na wannan duniya.