1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

MDD ta bukaci a tsayar da Isra'ila daga kai hari a Rafah

Zainab Mohammed Abubakar
February 12, 2024

Majalisar Dinkin Duniya ta ce yiwuwar kai cikakken kutsen da Isra’ila za ta yi a garin Rafah mai cunkoson jama’a abu ne mai ban tsoro, tare da barazanar haddasa jikkata mara adadi.

Hoto: MUNIR UZ ZAMAN/AFP

Babban jami'in kare hakkin bil'adama na  MDD Volker Turk ya bukaci manyan kasashen duniya da su dakatar maimakon ba da dama, yayin da firgicin kutsawa cikin yankin ke karuwa a tsakanin Falasdinawa sama da miliyan daya da suka makale a wannan yanki na kudu mai nisa.

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya sha alwashin tura sojojin kasa, zuwa yankin Rafah mai cunkoson jama'a a wani bangare na burinsa na kawar da kungiyar Hamas, abun da ya haifar da tsoro a duniya.

Yakin Gaza ya barke ne bayan da kungiyar Hamas ta kaddamar da wani hari da ba a taba ganin irinsa ba a Isra'ila a watan Oktoba wanda ya yi sanadin mutuwar mutane sama da dubu daya.

Yayin da kawo yanzu Isra'ila ke kan mayar da martani da hare hare ba kakkautawa a Gaza, wanda ya acewar ma'aikatar lafiyar yankin ya kashe sama da mutum du 28 galibi mata da kananan yara.