1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaJamus

MDD ta sake jan hankalin hukumomi a Sudan

December 4, 2021

Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira ga hukumomi a Sudan da su martaba 'yancin aikin jarida da na fadar albarkacin baki. Hukumomin kasar dai na ci gaba da tsare daruruwan jama'a.

Kolumbien UN-Generalsekretär Antonio Guterres
Hoto: Luisa Gonzalez/REUTERS

Sakatare Janar na Majalisar ta Dinkin Duniya, Antonio Guterres, shi ne ya nuna wannan bukata cikin wani rahoto da aka mika wa kwamitin sulhun majalisar a jiya Juma'a.

Daruruwan masu fafutukar siyasa da 'yan jarida da wasu da ke tsaye a gefen hanya aka tsare a Sudan, saboda zargin su da hukumomin kasar ke yi na kasancewa masu furjanye wa gwamnati.

Haka nan Majalisar Dinkin Duniyar, ta yi tir da amfani da harsasai masu kisa da jami'an tsaro ke yi a kan masu zanga-zangar nuna kin jinin gwamnati, abin da ke ci gaba da haddasa asarar rayuka a kasar.

A ranar 25 ga watan Oktoba ne dai Sudan din ta sake fadawa cikin sabuwar rigimar shugabanci, bayan kwace iko daga hannun firaminista Abdalla Hamdok da jagoran soji Janar Abdel Fattah al-Burhan ya yi.