MDD ta tsawaita takunkumin hana sayar da makamai a Darfur
September 12, 2025
Kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya tsawaita takunkumin hana sayar da makamai ga yankin Darfur na kasar Sudan da shekara guda. A kuduri da daukacin mambobi suka amince da shi, Majalisar ta tsawaita har zuwa ranar 12 ga Satumba 2026 da tsarin takunkumin da aka kakaba a 2005, wanda ya shafi daidaikun mutane biyar da aka hana tafiye-tafiye, da hana shigo da makamai a Darfour.
Karin bayani: Sudan: Matsalar jin-kai saboda yaki
Jakadan Amurka John Kelley ya ce wannan matakin na aike da sako karara cewar kasashen duniya na ci gaba da jajircewa wajen dakile kwararar makamai da kuma tabbatar da ganin an hukunta wadanda ke da hannu wajen haddasa tashe-tashen hankula a Darfur.
Sai dai a cewar majiyoyin diflomasiyya, wasu kasashe sun nuna dacewar fadada takunkumin hana sayar da makamai zuwa yankin Kordofan, amma kasar Rasha ta nuna adawa da matakin a matsayin mai kujerar na-ki a MDD.
Karin bayani: Sudan: Al'umma na cikin mawuyacin hali
A halin yanzu dai, yaki da ke wakana tsakanin sojoji karkashin Janar Abdel Fattah al-Burhan, da dakarun RSF na tsohon mataimakinsa Janar Mohamed Hamdan Daglo, na lamshe rayukan duban mutane tare da raba miliyoyi da matsugunansu.