1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Masu sa ido daga MDD za su je Yemen

Yusuf Bala Nayaya
January 16, 2019

Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya amince da shirin tura masu sanya idanu 75 zuwa birnin Hodeidah da ke gabar teku a Yemen ta yadda za su tsaya a birnin tsawon watanni shida su sa idanu kan tsagaita bude wuta.

Jemen UN-Beobachtermission l Ankunft von Patrick Cammaert
Hoto: Reuters/F. Salman

Bayan mako guda da tattaunawar zaman lafiya da aka yi a Sweden a watan da ya gabata, mayakan na Houthi da ke samun goyon baya na kasar Iran da dakarun sojan kasar ta Yemen da ke samun goyon bayan kasar Saudiyya sun zauna inda aka cimma yarjejeniyar zaman lafiya kan birnin na Hodeidah da ke zama mai muhimmanci kan harkoki na kasuwanci da hanyar samun abinci da kayan agaji ga miliyoyin al'umma a kasar ta Yemen da ke gargara ta fadawa hali na yunwa.

Sakataren MDD Antonio Guterres ya ce masu sa idon su 75 za su sa ido kan yarjejeniyar karkashin aikin da aka kira shi aikin MDD don tallafa wa yarjejeniyar Hodeidah (UNMHA).