1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: Gargadi bayan sassauata dokar Corona

Gazali Abdou Tasawa
May 11, 2020

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta yi kira ga Jamusawa da su yi taka tsan-tsan da kuma ci gaba da mutunta matakin sanya tazara a tsakaninsu da kuma saka takunkumi domin kauce wa komawa gidan jiya.

Berlin - Angela Merkel
Hoto: Reuters/M. Sohn

Shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel ta yi kira ga Jamusawa da su yi taka tsan-tsan da kuma ci gaba da mutunta matakin sanya tazara a tsakaninsu da kuma saka takunkumi domin kauce wa komawa gidan jiya.

Wannan na zuwa ne kwanaki kalilan bayan sassauta dokar kulle da takaita zirga-zirga bayan annobar Coronavirus ta soma ja da baya a kasar. Merkel ta yi wannan gargadi ne a karshen wani taro da ta gudanar ta bidiyo da hukumomin kiwon lafiya na kasar a wannan Litinin. Gwamnatin kasar ta Jamus ta sanar da ware kudi Euro miliyan 750 domin taimakawa ga aikin binciken samo allurar yaki da cutar ta COVID-19.

Alkalumman wannan Litinin dai sun nunar da cewa mutane kusan dubu 173 suka kamu da cutar ta COVID-19 a kasar ta Jamus inda ta halaka mutane sama da dubu bakwai da 580 a yayin da wasu dubu 143 suka warke.