1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaGabas ta Tsakiya

Ministan harkokin wajen Isra'ila ya kai ziyara Somaliland

Mouhamadou Awal Balarabe
January 6, 2026

Ba a bayyana dalilin ziyararsa a Hargeisa ba, amma Gideon Saar ya je Somaliland kasa da wata guda bayan da Isra'ila ta amince da ita a hukumance a 26 ga Disamban 2025 a matsayin kasa mai cin gashin kanta.

Ministan harkokin wajen Isra'ila Gideon Saar
Ministan harkokin wajen Isra'ila Gideon Saar Hoto: Emmanuel Dunand/Pool Photo/AP/picture alliance

Duk da ci gaba da daukanta da Somaliya ke yi a matsayin wani yankinta, amma ministan harkokin wajen Isra'ila Gideon Saar ya isa Somaliland a wannan Talatar, kasa da makonni biyu bayan da kasarsa ta amince da kasar da ta ayyana kanta a matsayin 'yantanta.

 Sanarwar da ta fito daga fadar shugaban kasar Somaliland ta ce tawagar ta Isra'ila ta sauka a Hargeisa babban birni, inda jami'an gwamnatin Somaliland suka tarbe ta a filin jirgin sama.

Karin bayani: Habasha za ta amince da 'yancin Somaliland

Ita dai  Isra'ila ta amince da Somaliland a hukumance a ranar 26 ga Disamban 2025 a matsayin kasa mai cin gashin kanta, mtakin da ke zama farau tun bayan ballewarta daga Somaliya a shekarar 1991.