Morocco ta samu tsallakawa zuwa zagaye na gaba na AFCON

A gasar cin kofin nahiyar Afirka ta bana da ke gudana yanzu haka a kasar Morocco, an fara shiga matakin yada kanin wani, inda mai masaukin baki Morocco ta samu nasarar tsallakawa zuwa zagaye na gaba, bayan lallasa Zambia da ci 3-0 a daren Litinin.
Haka zalika Afirka ta Kudu ma ta shiga wannan zagaye na 'yan 16, bayan doke Zimbabwe da 3-2.
Sai Mali da ta tsallake rijiya da baya wajen tsallake siradi, inda ta tashi canjaras da Comoros babu ci a tsakaninsu, wato 0-0.
Karin bayani:
'Yan wasan Bundesliga da ke bugawa a AFCON 2025
Ibrahim Maza na Leverkusen, Ellyes Skhiri na Frankfurt da Yan Diomande na Leipzig: 'Yan wasa da yawa da ke bugawa a Jamus sun shiga gasar cin kofin Afirka a Maroko. Amma ba wai kawai don sun zama taurari a Bundesliga ba.
Nicolas Jackson - FC Bayern Munich
Bai yi fice a watanni shidan farko da ya yi a Munich ba. Dan wasan da aka aro daga Chelsea, ya fi zama a benci, kuma ya taka leda ne kawai a matsayin wanda ya maye gurbin Harry Kane. Amma dan wasan mai shekaru 24, yana da cikakken gurbi a kungiyar kwallon kafa ta Senegal inda yake wasa da tsohon dan wasan Bayern Sadio Mané. Jackson ya buga a gasar AFCON ta 2024, inda aka cire Senegal da wuri.
Edmond Tapsoba - Bayer 04 Leverkusen
Dan wasan baya mai buga wa Burkina Faso kwallo a gasar AFCON. Ya buga wasanni sama da 200 a Leverkusen kuma ya lashe kofuna biyu da ita a 2024. Dan wasan mai shekaru 26 ya fara taka wa kungiyar kwallon kafar Burkina Faso tun yana shekaru 17, kuma tun daga lokacin ya buga wasanni sama da 50 a kasarsa. Amma, kwazonsa ya kare a zagaye na biyu a gasar cin kofin kasashen Afirka a 2024.
Cyriaque Irie - SC Freiburg
Shi ma Cyriaque Irie na SC Freiburg yana cikin tawagar Burkina Faso. Dan wasan gaba mai shekaru 20 ya samu damar buga wasanni na 'yan mintuna kadan a gasar Bundesliga ya zuwa yanzu, inda ya buga wasa daya kawai. Amma duk da haka, Irie ya ya zura kwallaye biyu ga kasarsa a wasanni hudu na farko na kasa da kasa.
Ramy Bensebaini - Borussia Dortmund
Ana daukar dan wasan Dortmund a matsayin ginshikin tsaro a kungiyar Aljeriya. Bisa wasanni 76 na kasa da kasa da wasanni sama da 275 a Ligue 1 ta Faransa, da Bundesliga (a Borussia Mönchengladbach da Borussia Dortmund) da kuma a gasar Turai, dan wasan mai shekaru 30, yana cikin 'yan wasa mafi kwarewa a kungiyarsa, da aka cire a matakin rukuni na gasar AFCON ta karshe a watan Janairun 2024.
Ibrahim Maza - Bayer 04 Leverkusen
Abokin wasan Bensebaini "Ibo" Maza (a hagu), dan wasa ne da ke matsa kaimi da jure wa matsin lamba. Ɗan wasan tsakiya ne da aka haifa a Berlin, amma kwanan nan ya burge Leverkusen, a matsayin dan wasan tsakiya na baya ko na tsakiya. A watan Nuwamba, an zabi dan wasan mai shekaru 20 a matsayin gwarzo a rukunin matasan 'yan wasan Aljeriya a bana.
Christian Kofane - Bayer 04 Leverkusen
Baya ga zakakurin dan wasa Maza, Leverkusen za ta ci gaba da wasanninta na gaba ba tare da Christian Kofane ba. Dan wasan mai shekaru 19 ya koma Leverkusen daga wata kungiya da ke lig na biyu na Spain a bazara ta 2025, kuma ya buga wasanni kusan 50 a rayuwarsa. Har yanzu yana jiran fara wasa a kungiyar Indimotable Lions ta kasar Kamaru. Amma dai mai horaswa ya kira dan wasan.
Eliesse Ben Seghir - Bayer 04 Leverkusen
Abokin aikin Kofane na Leverkusen yana cikin wadanda aka fi hasashen ya lashe gasar cin kofin Afirka a Maroko. Kungiyar "Lions de L'Atlas" na fatan daga kofinta na biyu baya ga na 1976, inda wasanta na karshe shi ne a 2004 a Tunisiya. Ben Seghir har yanzu na neman yin tasiri a Bundesliga, amma dan wasan mai shekaru 20 na taka leda akai-akai a gefen hagu na kasarsa.
Bilal El Khannouss - VfB Stuttgart
Yayin da aka haifi Ben Seghir kuma ya girma a kudancin Faransa, shi kuwa dan wasan VfB Stuttgart El Khannouss, dan Beljiyam ne, kasar da ya bugawa shekaru da yawa a rukunin matasa. A 2021, ya koma cibiyar samun horo ta Maroko. A 2024, dan wasan tsakiya mai kai hari ya shiga gasar cin kofin Afirka, amma kungiyarsa ta sha kashi a hannun Afirka ta Kudu. Yana da burin lashe gasar AFCON ta bana.
Samuel Essende - FC Augsburg
Samuel Essende, yana da karancin samun damar daukar kofi a ranar 18 ga Janairu. Dan wasan gaba na Augsburg da kungiyarsa ta Jamhuriyar Dimukuradiyyar Kwango ba sa cikin wadanda ake kyautata wa zato. Amma akwai yiwuwar isa mataki na gaba. Essende da abokan wasansa za su fafata da babbar kungiyar Senegal a rukuninsu, da kuma Benin da Botswana, wadanda aka raina su.
Mohamed Amoura - VfL Wolfsburg
Mai shekaru 25, shi ne babban dan wasan da ya fi zura kwallaye a Wolfsburg, inda yake da kwallaye shida a wasanni 14 na Bundesliga. Mai tsayin mita 1.70, dan wasan gaba yana taka rawar gani a fannin kai hari, kuma ya kware wajen yanke 'yan wasa. Yana wakiltar kasarsa ta Aljeriya a gasar AFCON na 2025 tare da Ibo Maza da Ramy Bensebaini.
Fares Chaibi - Eintracht Frankfurt
Fares Chaibi yana cikin tawagar Aljeriya. Dan wasan tsakiya da aka haifa a Faransa, ya fara buga wa "Fennecs" wasa a 2023. Ya buga wasa akai-akai a wasannin share fagen shiga gasar cin kofin duniya ta 2026, amma a matsayin mai maye gurbi. A Frankfurt, dan wasan mai shekaru 23 ya taimaka wajen cin kwallo sau shida a wannan kakar, shi ne babban dan wasan Eintracht.
Yan Diomande - RB Leipzig
Dan wasan ya yi tasiri a Leipzig saboda cin kwallaye bakwai da taimakawa a ci kwallaye 15. Wasannin kasa da kasa guda hudu kacal matashin ya yi a karkashin Côte d' Ivoire da ke rike da kambun AFCON. Amma a gasar Maroko ta cin kofin kasashen Afirka, dan kwallon mai shekaru 19 zai buga wasa tare da tsohon dan wasan Bundesliga Sebastien Haller da wani dan wasan Bundesliga na yanzu...
Amadou Haidara - RB Leipzig
Duk da cewar dan wasan tsakiya bai buga wa kungiyarsa kwallo a kakar 2025 ba, amma kocin kasar Mali ya dauke shi a gasar AFCON. Haidara mai shekaru 27, wanda ya fito daga Bamako ya yi wasanni 46 a kasashen waje, wannan zai zama gasar AFCON ta uku, baya ga na 2019 da 2022. Amma har yanzu Mali ba ta taba lashe gasar nahiyar Afirka ba.
Ibrahima Sissoko - VfL Bochum
Bayan sa ya buga wa kasar haihuwarsa Faransa a matakan 'yan kasa da shekara 18 zuwa 'yan kasa da shekara 21, dan wasan tsakiya ya yanke shawarar wakiltar kasar iyayensa, inda yake buga wa Mali wasa tun 2024. Yana halartar gasar AFCON ta farko a Maroko. Amma ba a zaɓi abokin wasansa na Bochum kuma takwaransa Ibrahim Sissoko ba a wannan karon.
Elias Saad - FC Augsburg
An haifi Saad (a hagu) a Hamburg, kuma da farko ya buga wa kungiyar kwallon kafar Jamus wasa a wasan Futsal kafin ya zama kwararren dan kwallon kafa, tare da fara buga wa kungiyar kwallon kafa ta Tunisiya wasa a 2024. Dan wasan mai shekaru 25 mai kai hari ya rasa matsayinsa na dindindin a Bundesliga, amma yana wasa a gefen hagu.
Ellyes Skhiri - Eintracht Frankfurt
Koda yake shi dan Faransa ne daga bangaren uwa, amma dan wasan Frankfurt na bugawa Tunisiya, kasar mahaifinsa. Skhiri ya halarci gasar cin kofin duniya ta 2018 da 2022 tare da Tunisia. Gasar cin kofin kasashen Afirka da ake yi a Maroko ce ta huɗu da dan wasan mai shekaru 30 ke halarta. Da wasanni sama da 70 na kasashen duniya, yana daya daga cikin 'yan wasa mafi kwarewa a kungiyarsa.
Stanley Ratifo - BSG Chemie Leipzig
Sabanin tokororinsa na Bundesliga, shi kadai ne dan wasa "da ba za a iya maye gurbinsa ba". Chemie Leipzig ya zura kwallaye 16 a gasar Regionalliga Nordost da ke rukuni na hudu, inda Ratifo ya zira kwallaye tara daga cikinsu. Yanzu yana bugawa Mozambik wasa a gasar cin kofin kasashen Afirka. Amma hutun Regionalliga yana ci gaba zuwa farkon Fabrairu, dan wasan mai shekaru 31 zai dawo kan lokaci.
Masar na sahun farko wajen shiga zagayen 'yan 16.
Najeriya wadda tuni ta shiga wannan mataki, a wannan Talata za ta yi wasanta na karshe a rukuni, inda za ta fafata da Uganda.
Sai wasa tsakanin Jamhuriyar Benin da Senegal.