1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaMaroko

Zanga-zangar kawo sauyi ta bar baya da kura a Morocco

Abdoulaye Mamane Amadou
October 1, 2025

Hukumomi a Morocco sun kama daruruwan mutane da suka fito zanga-zangar neman sauyi a yankuna da dama na gabashi da kudanci kasar

Jami'an tsaro sun kama masu zanga-zangar neman kawo saui a Morocco
Jami'an tsaro sun kama masu zanga-zangar neman kawo saui a MoroccoHoto: Abdel Majid Bziouat/AFP/Getty Images

Fiye da mutane 400 ne suka shiga hannun hukuma a Morocco, wasu sama da 300 kuma suka jikkata sakamakon tarzomar da ta barke a daren Talata a wasu manyan birane, kamar yadda ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ta sanar.

'Yan tawayen Mali sun saki direbobin Morocco da suka kama

Masu aiko da rahotanni sun ce masu zanga-zangar da suka yi arangama da jami'an tsaro, na bukatar ne a gudanar da sauye-sauye a fannoni da dama ciki har da na kiwon lafiya da ilimi.

Arangamar ta fi kamari ne a yankunan Oujda da ke gabashi, da kuma Inzegane na wajen birnin Agadir a kudanci, inda masu zanga-zangar suka yi artabu da jami'an tsaro.

Morocco ta ceto 'yan cirani sama da 800

Mai magana da yawun ma'aikatar cikin gidan Morocco Rachid El Khalfi, ya ce masu boren sun yi amfani da makamai ciki har da wuka da masu da ma wasu ababen fashewa don mayar wa 'yan sandan kwantar da tarzoma martani.