1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mulkin Burkina Faso a hannun matashin soja

October 6, 2022

Matasa a Burkina Faso na fatan matashin soja dan shekaru 34 da ya kifar da gwamnatin mulkin soja a kasar, zai kawo wa kasar ci gaba duk da yadda duniya ke Allah wadai da juyin mulkin.

Matashin soja  Ibrahim Traore mai shekaru 34 da ya kifar da gwamnati a Burkina Faso
Matashin soja Ibrahim Traore mai shekaru 34 da ya kifar da gwamnati a Burkina FasoHoto: RADIO TELEVISION BURKINA FASO/REUTERS

Majalisar dokokin ta bayyana bukatar hanzarta daukar matakan ladabtarwa da ma katse hanzarin masu yin mulki da sannu a hankali ke kara yin kutse ga mulkin dimukuradiyya a kasashen Afrika ta Yamma domin zama darasi ga 'yan baya. 

Masharhanta na bayyana cewa rashin daukar tsauraran matakai a kan masu juyin mulki na kara bude kofa ne kawai ga tsagerun sojoji da ke amfani da karfin bindiga wajen kifar da gwamnatin dimukuradiyya.

Tsallake zuwa bangare na gaba Rahotanni da Sharhuna