1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 22 sun mutu a turmutsitsi a Indiya

Salissou Boukari
September 29, 2017

Akalla mutane 22 ne suka mutu a wannan Juma'a a birnin Bombay na kasar Indiya sakamakon wata turarreniya da aka fuskanta a wata tashar jiragen kasa a cewar hukumomin kasar.

Bahnhof in Mumbai
Tashar jirgin kasa a birnin Bombay na IndiyaHoto: DPA

An dai samu turmutsitsin ne a lokacin da wani tarin jama'a suke kokarin sauka daga wata matattatakala da ke zuwa tashar jiragen kasa ta Elphinstone. Babban daraktan asibintin KEM inda aka kai mutanen da suka jikkata Avinash Supe, ya ce sun kidaya gawarwaki 22. Mai magana da yawun tashoshin jiragen kasa na kasar ta Indiya ya ce mutanen da ke nemen shiga jirgin, sun bi wannan hanya ce gabaki dayansu a kokarinsu na gujewa ruwan sama kamar da bakin kwarya da ke sauka a daidai lokacin. Cikin wani sako da ya aike ta shafinsa na Tweetter Firaministan kasar ta Indiya Narendra Modi ya nuna alhininsa tare da isar da ta'azziya ga iyalan marigayan.