1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 31 sun rasu a wani hari a China

May 22, 2014

Fashewar wasu abubuwa a wata kasuwa da ke Urumki a lardin Xinjiang na yammacin China sun yi sanadiyyar rasuwar mutane 31 yayin da wasu sama da casa'in suka jikkata.

Messerattacke in Changsha China
Hoto: Reuters

Gidan talabijin din China na CCTV ya ce an jefa abubuwan fashewar ne cikin kasuwar daga cikin wasu motoci, yayin guda daga cikin motocin da ke makare da abubuwan na fashewa ta tarwatse.

Tuni dai baban jami'in tsaron kasar da ke yankin da abin ya faru ya danganta harin a matsayin na ta'addanci, yayin da kamfanin dillancin labarai na China na Xinhua ya rawaito shugaban kasar na cewar gwamnati za ta hukunta wanda aka samu da hannu wajen kai harin kuma ta lashi takobin tabbatar da zaman lafiya a yankin.

A baya dai gwamnatin China ta sha danganta tada kayar bayan da ake samu a yankin da harin na yau ya wakana da 'yan awaren da ke Xinjiang din.

Mawallafi: Ahmed Salisu
Edita: Usman Shehu Usman