1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane 8 sun mutu a hare-hare a Somaliya

Abdul-raheem Hassan MAB
June 15, 2019

Wasu tagwayen hare-haren kunar bakin wake sun kashe mutane da dama a Somaliya babban birnin kasar Somaliya. Tuni 'yan ta'adda na al Shabaab sun dauki alhakin hare-haren.

Somalien Bombenanschlag in Mogadischu
Hoto: picture-alliance/AP Photo/F. Abdi Warsameh

Mayakan al-Shabaab sun dauki alhakin harin kunar bakin wake da ya kashe mutane akalla 8 tare da jikkata wasu da dama a kusa da ginin majalisar dokokin kasar a wannan Asabar. Wadanda suka shaidar da harin na cewa bam din ya rusa shaguna da gidajen mutane da dama. Rahotanni sun ce an kuma samun tashin wani bam a babban titin zuwa filin jirgin sama da ke babban birnin kasar Mogadishu, Sai dai babu rahotannin asarar rayuka a harin na biyu. 

'Yan sanda sun killace dukkannin titunan da suka hade da wurin da aka kai hare-haren, jami'an agajin gaggawa kuma na ci gaba da ayyukan ceto. Tun dai ba yau ba mayakan al-Shabaab da ke ikirarin zama reshen kungiyar al-Qa'ida na zama barazana ga rayuwar fararen hula tun bayan da kungiyar ta lashi takobin ganin bayan gwamnati.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW