1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Mutane da dama sun mutu a wani sabon rikici a Chadi

May 15, 2025

Ana yawan samun tashin hankali a lardunan kudancin kasar Chadi musamman tsakanin kabilu da addinai da kuma makiyaya da manoma.

Shugaban Chadi Mahamat Idriss Déby Itno
Shugaban Chadi Mahamat Idriss Déby ItnoHoto: Mikhail Metzel/dpa/AP/picture alliance

Gwamnatin Chadi ta sanar da cewa wani sabon rikici ya halaka mutane akalla 35, duk da cewa hukumomin N'Djamena basu yi cikakken bayani dangane da rikicin ba.

Karin bayani:Ambaliya: Kwalara ta barke a Kamaru da Chadi 

Ministan Yada Labarai kuma kakakin gwamnati Gassim Cherif Mahamat ya kara da cewa mutane shida sun jikkata a yayin rikicin da ya afku a lardin Logone-Occidental. Ministan ya kara da cewa tuni jami'an tsaro suka shawo kan rikicin.