1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane da dama sun rasu a harin birnin Maiduguri

Salissou BoukariJune 4, 2015

Adadin mutanen da suka rasu a harin kunar bakin waken da aka Kai a birnin Maiduguri, ya kai na mutune 18 yayin da wasu da dama suka samu raunuka.

Selbstmordanschlag in Maiduguri, Nigeria
Hoto: AFP/Getty Images/Stringer

A yammacin jiya Laraba wani dan kunar bakin wake ya kai hari a wani garejin gyaran motoci da ke kallon wani barakin soja a birnin na Maiduguri inda kanikawa da dama suka rasu. A kokarin da ya ke na ganin bayan rikicin kungiyar Boko Haram, sabon Shugaban kasar ta Najeriya Muhammadu Buhari ya kai wata ziyara a kasar Nijar, inda ya tattauna da hukumomin kasar kan batun na tsaro a jiya Laraba.

A wannan Alhamis din kuma shugaban na Najeriya ya isa a birnin Ndjamena na kasar Chadi, inda ya Ghana da takwaransa na wannan kasa Idriss Deby da sojojin kasarsa ke taka rawa a yakin da ake da 'yan kungiyar ta Boko Haram. Ana sa ran daukan wasu sabin matakan yaki da 'yan kungiyar ta Boko haram nan bada jimawa ba.