Mutane sun mutu a rikicin zaben Indonesiya
May 23, 2019Talla
'Yan sanda sun tabbatar da mutuwar mutane bakwai a Jakarta babban birnin kasar Indonesiya bayan barkewar rikici sakamakon zanga-zangar lumana kan ayyana Shugaba Joko Widodo a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar.
Wannan dai shi ne karo na biyu da Shugaba Widodo ke kada abokin takararsa Prabowo a takarar shugabancin Indonesiya, amma 'yan adawa na zargin gwamnati ta amfani da ikonta wajen yin magudin zabe.