1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutane sun mutu a rikicin zaben Indonesiya

Abdul-raheem Hassan
May 23, 2019

'Yan sanda sun ce kura ta lafa a birnin Jakarta bayan kame daruruwan mutane da ake zargi da haddasa rikicin, amma akwai sauran kallo kan matakin dan takara Prabowo Subianto na kalubalantar sakamakon zaben.

Indonesien Nach den Anschlägen
Hoto: picture-alliance/AA/A. Raharjo

'Yan sanda sun tabbatar da mutuwar mutane bakwai a Jakarta babban birnin kasar Indonesiya bayan barkewar rikici sakamakon zanga-zangar lumana kan ayyana Shugaba Joko Widodo a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasar.

Wannan dai shi ne karo na biyu da Shugaba Widodo ke kada abokin takararsa Prabowo a takarar shugabancin Indonesiya, amma 'yan adawa na zargin gwamnati ta amfani da ikonta wajen yin magudin zabe.