1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Mutanen da suka mutu a Chemnitz sun karu

Mouhamadou Awal Balarabe
August 28, 2018

Yayin da 'yan sanda suka ce wadanda suka mutu a zanga-zangar sun kai 20, ministar shari'a ta Jamus ta yi gargadi game da daukar doka a hannu a rikicin da ke gudana a Chemnitz da ke gabashi,

Deutschland Demonstration der rechten Szene in Chemnitz
Hoto: picture-alliance/dpa/S. Willnow

Rundunar 'yan sandan Jamus ta bayyana yawan mutanen da suka jikkata a zanga-zangar kin jinin baki a garin Chemnitz na gabashin kasar daga mutane shida zuwa 20. Cikin wata sanarwa da ta fitar a wannan Talatar, rundunar ta ce 'yan sanda biyu, da masu akidar kyamar baki da masu zanga-zanga tara sun ji rauni a cikin rikicin.

Ministar shari'a ta Jamus Katharina Barley ta yi kira ga hukumomin Jihar Saxon da ke gabashin kasar da su c gaba da gurfanar da masu akidar kyamar baki da suka aikata laifukan a tashin hankalin da ya barke a garin Chemnitz. Tuni dai Jamusawa suka fara nuna fargaba dangane salon da zanga-zangar ke dauka.

 Mutuwar wani dan shekaru 35, wanda ake zargi wani da ke da tushe da Siriya da Iraki ne ta haddasa wannan tashin hankalin.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW