Mutum 33 sun halaka a hadarin jirgin ruwa a Najeriya
September 15, 2017Talla
A wata sanarwar da hukumar agaji ta NEMA shiyar Arewa maso Gabashin Najeriyan ta fitar, ta ce jirgin ruwan ya na dauke da mutane fiye da kima a yayin da hadarin ya auku, kuma baya ga mutane talatin da uku da aka yi nasarar zakulo gawarwakinsu daga cikin ruwa akwai wasu mutane ashirin da uku da suka bata, hadarin ya auku ne a safiyar wannan Laraba inji wani jami'in hukumar ta NEMA.