1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Miyanmar: An jibge tankokin yaki

February 16, 2021

Majalisar Dinkin Duniya ta gargadi sojoji a Miyanmar dasu mutunta yancin bil adama ko kuma su fuskanci fushinta.

Myanmar | Proteste nach Militärputsch
Hoto: AP/dpa/picture alliance

Bayan jibge tankokin yaki a wasu manyan titunan kasar Myanmar, Majalisar Dinkin Duniya ta yi wa sojojin juyin mulki a kasar albishir da mummunan mataki, saboda amfani da karfin da ya wuce kima a kan masu zanga-zangar adawa da juyin mulkin.

An samu raguwar masu zanga-zangar a jiya Litinin sakamakon motocin yakin da aka gani a manyan biranen kasar da aka yi wa damakaradiya karan tsaye.

Wani mai magana da yawun Majalisar Dinkin Duniya, Farhan Haq, ya tabbatar da wata ganawa da aka yi jiya a tsakanin wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya ta musamman a Myanmar da mataimakin jagoran 'yan juyin mulkin, inda ta bukace su da mutunta 'yancin dan Adam kuma ta gargade su da su kauce wa sake tsinke hanyoyin sadarwa.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW