1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shekaru 74 da kai harin nukiliya a garin Nagasaki

Ramatu Garba Baba
August 9, 2019

A wannan Juma'a aka yi taron tuni da kazamin harin nukiliya da Amirka ta kai kan birnin Nagasaki na kasar Japan da ya ya janyo asarar rayukan dubban mutane

Japan 74. Jahrestag Atombombenabwurf auf Nagasaki | Gedenken | Bürgermeister Tomihisa Taue
Hoto: Imago Images/Kyodo News

A wannan Juma'a,  Japan ke taron cika shekaru saba'in da hudu da Amurka ta kai wa birnin Nagasaki hari da makamin nukiliya. Magajin garin birnin Tomihisa Taue, ya baiyana takaici kan yadda kasashen Amirka da Rasha suka yi biris da kiran jama'ar da suka tsira daga harin suka yi, na daina kera makaman nukiliya. Ya gayyaci shugabanin kasashen duniya da su kawo ziyara kasar don gane wa idanunsu irin ta'asar da makamin ya haddasa.


Jama'a daga sassan kasar ne suka hallaci taron kafin a gudanar da addu'oi da kuma yin tsit na minti guda don girmama mamatan. Mutum fiye da dubu saba'in ne suka mutu a sanadiyar harin da Amirkan ta kai da makamin nukiliyan.