Najeriya: Alkalin Alkalai ya yi murabus
April 5, 2019Talla
Lauyan Mr. Onnoghen, Adegboyega Awomolo ne ya tabbatar da wannan labarin a hirarsa da kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP, inda ya ce tun a jiya ne Alkalin Alkalan ya ajiye aiki.
A kwanakin da suka gabata ne dai hukumar kula da harkokin shari'a ta kasar NJC ta bai wa Shugaba Muhammadu Buhari shawarar sauke Onnoghen din daga bakin aiki, wanda a halin yanzu ya ke fuskantar shari'a a gaban kotun da'ar ma'aikata kan batun bayyana kadarorinsa.