1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Bala'iNajeriya

Ko za a kawo karshen ambaliya a Najeriya?

Lateefa Mustapha Ja'afar
May 30, 2025

Rahotanni daga Najeriya na nuni da cewa, adadin wadanda suka rasa rayukansu sakamakon ibtila'in ambaliyar ruwa da ya afku a garin Mokwa na jihar Niger a Arewa maso Tsakiyar kasar na karuwa.

Najeriya | Niger | Mokwa | Ambaliyar Ruwa
Ibtila'in ambaliyar ruwa ya halaka mutane a jihar Niger da ke tsakiyar NajeriyaHoto: OLYMPIA DE MAISMONT/AFP/Getty Images

Kakakin Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar Niger SEMA Ibrahim Audu Husseini ne ya shaidawa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa, adadin ya kai sama da 100 bayan da aka sake gano gawarwakin mutane. Hukumar ta SEMA ta sanar da cewa mamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka kwashe tsawon daren Larabar wannan mako ana yi, ya yi awon gaba da gidaje sama da 50 a birnin na Mokwa da ke tsakiyar jihar ta Niger. Da ma dai Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya NIMET ta yi gargadin samun mamakon ruwan sama a jihohi 15 na kasar, cikinsu har da jihar ta Niger.