Najeriya: An sace 'yan mata a Yobe
February 22, 2018Talla
Duk da cewa gwamnatin Tarayyar Najeriyar ta musanta zancen sace 'yan matan 'yan makarantar sakandare a jihar Yobe, sai dai mahukuntan jihar ta Yobe sun sanar da cewa jami'an tsaro sun fafata da mayakan na Boko Haram tare da ceto wasu daga cikin 'yan matan. A baya dai gwamnatin Tarayya Najeriya ta nunar da cewa sojojin kasar na samun nasara a yakin da suke da mayakan na Boko Haram da suka addabi Najeriyar dama wasu makwabtanta.